Shugaba Joe Biden ya zafafa sukar da yake yi wa Donald Trump, inda yake zargin sa da shirin keta haddin kundin tsarin mulkin Amurka.
Ya kuma bayyan cewa tsohon shugaban da magoya-bayansa na da haÉ—arin gaske ga dimokuradiyya.
A cikin yanayi na barazanar dakatar da harkokin gwamnati a cikin kwanaki muddin majalisa ba ta amince da a karÉ“i karin kudade bashi ba, Mista Biden ya ce hatta a cikin jam’iyyar Republican akwai masu tsattsauran ra’ayi da ke harzuka juna.
Ya ce “Dimokuradiyya ta al’umma ce, ba sarauta ba ce ko abin neman kuÉ—i, ba tare da alaÆ™a da bangaranci jam’iyya ba, akwai bukatar yarda da shan kaye da rungumar Æ™addara.”
Ya kuma ce kokarin da Mista Trump ke yi na sake neman kujerar shugabancin Amurka, buri ne kawai da ke cike da mugun nufi na ramuwar gayya