Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya ce zai koyawa sauran jam’iyyun siyasa a jihar mumunan darasi a zaben 2023.
Fintiri ya bayyana haka ne a lokacin da kungiyar kansilolin jihar Adamawa ta amince da shi a matsayin dan takaranta a dakin liyafa na gidan gwamnati da ke Yola wanda ya gudana a ranar Laraba.
Ya ce“Sun gaza a cikin shekaru hudu da suka samu damar gudanar da mulkin jihar, kuma ba za mu bari su yaudari jama’armu ba, za mu ci gaba da in aiki tukuru, mu samar da ribar dimokuradiyya. A kan haka, na yi imani, za mu koya musu darussa marasa kyau, cewa za su rasa dukkan zabukan daga shugaban kasa zuwa matsayi na karshe a cikin al’umma, wato na kansila,” inji Fintiri.