fidelitybank

Siyasa: Ganduje ya magantu a kan rikicin G7

Date:

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da martani kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyarsa ta APC a Kano, wanda ya yi sanadiyar raba jam’iyyar zuwa gida biyu a jihar.

Da yake magana a wata hira da RFI Hausa a ranar Laraba, Ganduje ya ce fiye da shekaru 40 da ya yi a fagen siyasa, halin da Kano ke ciki yanzu ba abin damuwa ba ne.

“Halin da ake ciki a siyasa na saba gani. Kuma ko da yaushe akwai yuwuwar rarrabuwar kawuna, haka ma kuma akwai na sulhu, domin haka dukkan mu a bangarorin biyu kwararrun ‘yan siyasa ne, kuma mun yi irin wadannan abubuwan. Saboda haka jam’iyyar mu ta kasa ta dukufa wajen ganin an shawo kan rikicin, amma abin da nake kokarin bayyanawa a nan shi ne cewa, mu ba sababbi ba ne a siyasa, kuma ba kawai mun shiga ciki ba. Na shiga siyasa tun sama da shekaru 40 da suka wuce, ban da haka kuma na yi karatun siyasa a jami’a, kuma abin da mu ke yi ke nan”. Inji Ganduje.

Rikicin dai ya biyo bayan kammala taron da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar Kano, wanda ya kai ga raba jam’iyyar gida biyu tsagin Dr Abdullahi Umar Ganduje da kuma na Malam Ibrahim Shekarau.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp