Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da martani kan rikicin da ya dabaibaye jam’iyyarsa ta APC a Kano, wanda ya yi sanadiyar raba jam’iyyar zuwa gida biyu a jihar.
Da yake magana a wata hira da RFI Hausa a ranar Laraba, Ganduje ya ce fiye da shekaru 40 da ya yi a fagen siyasa, halin da Kano ke ciki yanzu ba abin damuwa ba ne.
“Halin da ake ciki a siyasa na saba gani. Kuma ko da yaushe akwai yuwuwar rarrabuwar kawuna, haka ma kuma akwai na sulhu, domin haka dukkan mu a bangarorin biyu kwararrun ‘yan siyasa ne, kuma mun yi irin wadannan abubuwan. Saboda haka jam’iyyar mu ta kasa ta dukufa wajen ganin an shawo kan rikicin, amma abin da nake kokarin bayyanawa a nan shi ne cewa, mu ba sababbi ba ne a siyasa, kuma ba kawai mun shiga ciki ba. Na shiga siyasa tun sama da shekaru 40 da suka wuce, ban da haka kuma na yi karatun siyasa a jami’a, kuma abin da mu ke yi ke nan”. Inji Ganduje.
Rikicin dai ya biyo bayan kammala taron da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar Kano, wanda ya kai ga raba jam’iyyar gida biyu tsagin Dr Abdullahi Umar Ganduje da kuma na Malam Ibrahim Shekarau.