fidelitybank

Sinadaren haɗa Bam ne suka fashe a Kano – Ƴan sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, ta ce, fashewar da ta auku a wani shago a unguwar Sabon Gari a ranar Alhamis 17 ga watan Mayu, wadda ta hallaka mutum tara, ta faru ne a sanadiyyar wasu sinadarai da ake iya hada bam da su.

A lokacin da fashewar ta auku an rika yada labari masu karo da juna dangane da musabbabin abin, inda wasu ke cewa bam ne ya tashi wasu kuma ke cewa tukunyar gas ce ta mai aikin walda ta fashe a shagon.

A tattaunawarsa da wakilin BBC a wurin da fashewar ta auku, a ranar, Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar ta Kano, CP Sama’ila Dikko, ya ce, tukunyar gas da ake walda da ita a wajen ce ta fashe, “amma ba bam ne ya tashi ba kamar yadda ake faɗa.”

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan-sandan Jihar SP Abdullahi Kiyawa, ya fitar a ranar Asabar 21 ga watan Mayu, 2022, rundunar ta ce, mutumin da yake gudanar da haramtaccen kasuwancin na sayar da wadannan haramtattun sinadarai, wadanda ake hada bam da su, da aka gano, Michael Adejo, ya mutu a fashewar.

Sanarwar ta ce, ”Binciken farko-farko ya nuna cewa daga cikin mutum tara da fashewar ta rutsa da su, daya daga cikinsu yana ajiye sinadarai masu lahani da sauran abubuwa masu hadari ba bisa ka’ida ba.

Mutum shi ne Michael Adejo, (wanda ya mutu).”

Rundunar ‘yan-sandan a wannan sanarwa ta ranar Asabar ta tabbatar da mutuwar mutum tara da kuma wasu takwas wadanda suka hada da dalibai da ta ce sun samu ‘yan raunuka a sanadiyyar fashewar ta ranar Talata.

‘Yan-sandan sun bayyana sunayen wadanda suku mutum kamar haka, Ejike Vincent (mai walda) da Michael Adejo (mai sayar da sinadarai) da Musa Kalla (mai sayar da shayi da Christiana Abosade da Mary da Austine Dada da Madam Owoleke da Omo Ben da kuma Bose Oladapo.

Rundunar ta kuma bayyana wasu tarin durum-durum da jarkoki da ke dauke da sinadarai iri daban-daban, masu hadari da ta ce ta gano a inda lamarin ya faru.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp