fidelitybank

Shugabar ƙasar Hungary ta sauka daga kujerar ta bayan da ta zargi wani da yin lalata

Date:

Shugabar ƙasar Hungary, Katalin Novak, ta ajye aikinta saboda maganganun da suka taso bayan afuwar da ta yi wa wani mutum da aka samu da laifin alaƙa da zarafi ta hanyar lalata.

A makon da ya gabata ne shugabar ƙasar ta yi wa mutumin da aka ɗaure a gidan ayarin ƙasar afuwa, bayan kotu ta same da laifin tilasta wa ƙananan janye iƙirarin cin zarafi ta hanyar lalata da suke yi wa wani daraktan gidan kula da ƙananan yara.

Matakin afuwar ya janyo tarin zanga-zanga neman ta sauka daga muƙaminta.

Misis Novak ta nemi afuwar ‘yan ƙasar tana mai cewa ta yi ”kuskure” wajen yin afuwar.

Tsohuwar ministan shari’a Judit Varga – wadda ta sanya hannu kan takardar amincewa da afuwar – ita ta ajiye aikinta na jagorar yaƙin neman zaɓen jam’iyyar firaministan ƙasar Viktor Orban.

Ce-ce-ku-cen da ya janyo ta ajiye muƙamin nata na zuwa ne bayan da a makon da ya gabata kafar yaɗa labaran ƙasar ta wallafa sunayen mutum 25 da Misis Novak ta yi musu afuwa a watan Afrilun shekarar da ta gabata, a wani ɓangare na ziyarar Fafaroma Fransis zuwa ƙasar.

A cikin jerin sunayen ne aka ga sunan mataimakin daraktan gidan kula da ƙananan yara, da aka ɗaure shekara uku a gidan yari bayan samunsa da laifin tilasta wa ƙananan yara janye iƙirarin cewa daraktan gidan ya ci zarafinsu.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp