A yau Litinin shugabannin kasasshn Turai za su taru a birnin Paris na Faransa domin tattauna yakin Ukraine a matsayin martani ga shirin Shugaba Donald Trump na tattaunawa kai-tsaye da Rasha da nufin kawo karshen yakin.
Rahoton rashin gayyatar kasahsen Turai ko Ukraine kan a tattaunawar da za a yi a cikin makon nan a kasar Saudiyya ya jefa Turai cikin mamaki da bacin rai.
Wakilin BBC ya ce jami’ai a Faransa na son mayar da wannan taron gaggawar tamkar wanda aka saba yin sa,
Sannan taron wata dama ce ga shugabannin Turai domin tattaunawa da daukar matakin bai-daya wajen yin martani ga Mista Trump kan batun Rasha da Ukraine.