Shugabannin tsaro sun isa zauren majalisar dokoki a ranar Larabar domin mayar da martani ga kudirin majalisar dattawa na yin mu’amala da yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a kasar.
Sun isa zauren majalisar da misalin karfe 12:39 domin ganawa da kwamitin daukacin Sanatoci.
Gayyatar shugaban ma’aikatan dai ya biyo bayan rashin tsaro da ake fama da shi a kasar wanda Abuja, babban birnin tarayya ta yi wa kawanya.