fidelitybank

Shugabannin baya ba su yi wa ƴan Najeriya tanadi ba – Tinubu

Date:

Shugaba, Bola Tinubu, ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ke yi, tana yi ne da nufin gyara makomar yara masu tasowa.

Yayin da yake jawabi ga ƙungiyar ƴan majalisa ta uku – wadda ya kasance cikin a Jamhuriya ta uku – da suka kai masa ziyara a fadarsa, Shugaba Tinubu ya ce a baya ƙasar na kashe kuɗaɗen yaran ƙasar da ba a kai ga haihuwarsa ba.

“Shekara 50 da suka gabata, Najeriya na kashe kuɗaɗen yaran da ba a kai ga haihuwarsu ba, tare da mayar da hankali kan man fetur wajen samun kuɗin shiga. Ba a yi wani tsari na tallafa wa yaran da za a haifa a gaba ba,” kamar yadda ya ce.

Shugaban ya kuma bayyana tarin matsalolin da ya fuskanta a farkon mulkinsa, musamman fannin tattalin arzikin da rayuwar jama’a.

“Mun fuskanci tarin ƙalubale a lokacin da na karɓi mulki. Inda ba mu ɗauki matakai ba da yanzu ƙasar ta talauce, kuma ai haƙƙinmu ne mu kare tattalin arzikinmu daga rugujewa”, in ji Shugaba Tinubu.

To amma shugaban ya ce a yanzu kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu dangane da sauye-sauyen da gwamatinsa ta fara ɓullo da su.

“Amma a yau bayan shimfiɗa mai kyau da muka yi, mun smau nasarar magance matsalolin da suka tunkaro ƙasarmu, a yanzu canjin kuɗi ya daidaita, farashin abinci na ci gaba da sauka, musamman a lokacin Ramadan, da yardar Allah wahalar ta zo ƙarshe”, a cewar shugaban na Najeriya.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp