fidelitybank

Shugabanni sun mika saƙonnin jaje bisa mutuwar mutane 177 da jirgin sama ya fadi a Koriya

Date:

Shugabannin ƙasashen duniya sun soma aikewa da saƙonnin jaje ga gwamnatin Koriya da Kudu bisa hatsari jirgin saman da ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla 177.

Shugaban China, Xi Jinping na daga cikin mutanen da suka fara aikewa da ta’aziyyarsu ga iyalan mamatan.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa a Telegram, Mista Xi ya ce ya kaɗu matuƙa da hatsarin jirgin.

“A madadin gwamnati da al’ummar China, ina miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mutanen da suka mutu, tare da fatan samun sauƙi da waɗanda suka samu raunuka”, kamar yadda ya wallafa.

Shi ma sakataren wajen Birtaniya, David Lammy, ya ce labarin hatsarin jirgin ya tayar masa da hankali.

Cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Lammy ya jajanta wa mutanen ƙasar da na Thailand.

A baya hukumar kashe gobara ta Koriya ta Kudu ta aƙalla mutum 151 ne suka mutu a hatsarin jirgin saman ƙasar bayan da wani jirgin saman fasinja ya kauce daga titinsa yayin da yake sauka a filin jirgin sama a Koriya ta Kudu.

Hukumar kashe gobarar ta ce daga cikin wadanda suka mutu 71 maza ne, mamat 71 , yayain da suka kasa tantance jinsi gawawaki huɗu sakamakon ƙonewar da suka yi.

Jirgin dai na ɗauke da mutum 181, ciki har da ma’aikatansa shida a lokacin da hatsarin ya auku.

Jami’an agaji sun ceto ma’aikatan jirgin biyu, bayan faruwar lamarin.

Jirgin kirar Boeing 7-3-7 ya sauka, bayan dawowa gida daga Bangkok na ƙasar Thailand.

Saukar tasa ke da wuya ne ya kwace ya saki titinsa ya kutsa ta cikin wani gini, kana ya kama da wuta.

Shaidu sun ce sun ji karar fashewar wani abu mai karfi bayan faruwar lamarin. Sai dai kawo yanzu adadin ya karu.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp