Shugabannin ƙasashen duniya sun soma aikewa da saƙonnin jaje ga gwamnatin Koriya da Kudu bisa hatsari jirgin saman da ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla 177.
Shugaban China, Xi Jinping na daga cikin mutanen da suka fara aikewa da ta’aziyyarsu ga iyalan mamatan.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa a Telegram, Mista Xi ya ce ya kaɗu matuƙa da hatsarin jirgin.
“A madadin gwamnati da al’ummar China, ina miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mutanen da suka mutu, tare da fatan samun sauƙi da waɗanda suka samu raunuka”, kamar yadda ya wallafa.
Shi ma sakataren wajen Birtaniya, David Lammy, ya ce labarin hatsarin jirgin ya tayar masa da hankali.
Cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Lammy ya jajanta wa mutanen ƙasar da na Thailand.
A baya hukumar kashe gobara ta Koriya ta Kudu ta aƙalla mutum 151 ne suka mutu a hatsarin jirgin saman ƙasar bayan da wani jirgin saman fasinja ya kauce daga titinsa yayin da yake sauka a filin jirgin sama a Koriya ta Kudu.
Hukumar kashe gobarar ta ce daga cikin wadanda suka mutu 71 maza ne, mamat 71 , yayain da suka kasa tantance jinsi gawawaki huɗu sakamakon ƙonewar da suka yi.
Jirgin dai na ɗauke da mutum 181, ciki har da ma’aikatansa shida a lokacin da hatsarin ya auku.
Jami’an agaji sun ceto ma’aikatan jirgin biyu, bayan faruwar lamarin.
Jirgin kirar Boeing 7-3-7 ya sauka, bayan dawowa gida daga Bangkok na ƙasar Thailand.
Saukar tasa ke da wuya ne ya kwace ya saki titinsa ya kutsa ta cikin wani gini, kana ya kama da wuta.
Shaidu sun ce sun ji karar fashewar wani abu mai karfi bayan faruwar lamarin. Sai dai kawo yanzu adadin ya karu.