fidelitybank

Shugabanin ɓangarorin siyasa ku tallafawa Chadi – Buhari

Date:

Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya yi kira shugabanin ɓangarorin siyasa a Chadi da su nuna kishin ƙasa ta hanyar shiga harkokin mayar da ƙasar kan tafarkin dimokradiyya.

Yayin da yake magana da shugaban mulkin sojin ƙasar Janar Mehmet Idris Deby-Itno a wata ziyara da ya kai masa a gefe guda a taron Majalisar Dinkin Duniya da ake ci gaba da gudanarwa a birnin Doha na ƙasar Qatar ranar Lahadi.

Shugaba Buhari ya ce ”Ina ganin irin ci gaban da ake samu a ƙasarka, a matsayina na makwabci da batun ƙasarku nake kwana, kuma da shi nake tashi a zuciyata”, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Mallam Garba Shehu ya fitar.

“Na tausaya maka, ba wai dan kana matashi ba, sai dan saboda da matsayin da wasu ƙungiyoyin da ke ƙasashen waje irinsu Libya suke ɗauka, duk da cewa wannan matsala ce da ka gaje ta daga wajen mahaifinka”, in ji Buhari

Ya kamata sauran ƙungiyoyin da ke tunanin cewa suna da ƙarfi su bayar da haɗin kai domin ceto ƙasarsu.”

Shugaba Buhari ya gode wa shugaban mulkin sojin Chadin kan ziyarar da ya kai masa tare da tabbatar masa da cewa ”a matsayinka na makwabci a shirye nake kodayaushe wajen sauraron buƙatun shawarwarinka, kan siyasa da tsaro da sauran fannoni”.

A nasa ɓangare shugaban mulkin sojin Chadin ya gode wa shugaba Buhari kan goyon bayan da yake ba shi tare da ƙasarsa a yayin da ƙasar ke shirin komawa tafarkin dimokradiyya, wanda ya ce shirin na tafiya kamar yadda ya kamata.

Ya kuma yi wa Buhari fatan alkairi tare da taya shi murnar nasarar dimokraɗiyya a Najeriya, tare da cewa ”Muna fatan ci gaba da ganinka ko bayan saukarka daga mulki”.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp