Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya yi kira shugabanin ɓangarorin siyasa a Chadi da su nuna kishin ƙasa ta hanyar shiga harkokin mayar da ƙasar kan tafarkin dimokradiyya.
Yayin da yake magana da shugaban mulkin sojin ƙasar Janar Mehmet Idris Deby-Itno a wata ziyara da ya kai masa a gefe guda a taron Majalisar Dinkin Duniya da ake ci gaba da gudanarwa a birnin Doha na ƙasar Qatar ranar Lahadi.
Shugaba Buhari ya ce ”Ina ganin irin ci gaban da ake samu a ƙasarka, a matsayina na makwabci da batun ƙasarku nake kwana, kuma da shi nake tashi a zuciyata”, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Mallam Garba Shehu ya fitar.
“Na tausaya maka, ba wai dan kana matashi ba, sai dan saboda da matsayin da wasu ƙungiyoyin da ke ƙasashen waje irinsu Libya suke ɗauka, duk da cewa wannan matsala ce da ka gaje ta daga wajen mahaifinka”, in ji Buhari
Ya kamata sauran ƙungiyoyin da ke tunanin cewa suna da ƙarfi su bayar da haɗin kai domin ceto ƙasarsu.”
Shugaba Buhari ya gode wa shugaban mulkin sojin Chadin kan ziyarar da ya kai masa tare da tabbatar masa da cewa ”a matsayinka na makwabci a shirye nake kodayaushe wajen sauraron buƙatun shawarwarinka, kan siyasa da tsaro da sauran fannoni”.
A nasa ɓangare shugaban mulkin sojin Chadin ya gode wa shugaba Buhari kan goyon bayan da yake ba shi tare da ƙasarsa a yayin da ƙasar ke shirin komawa tafarkin dimokradiyya, wanda ya ce shirin na tafiya kamar yadda ya kamata.
Ya kuma yi wa Buhari fatan alkairi tare da taya shi murnar nasarar dimokraɗiyya a Najeriya, tare da cewa ”Muna fatan ci gaba da ganinka ko bayan saukarka daga mulki”.