fidelitybank

Shugaban ƙasar Sudan ya kori mataimakin sa da suke gwabza faɗa

Date:

Babban hafsan sojojin Sudan Laftanar-Janar Abdel Fattah al-Burhan ya kori mataimakinsa kuma kwamandan dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti.

Dukkanin Janar Burhan da Hemedti sun yi aiki a matsayin shugaba da mataimakin majalisar mulkin soji, tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Oktoban 2021.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Janar Burhan ya naɗa tsohon madugun ‘yan tawaye Malik Agar a matsayin mataimakinsa.

Mista Agar memba ne na Majalisar mulkin sojin ƙasar.

Ya umurci sakatariyar majalisar mulki da hukumomin jihar da su gaggauta aiwatar da wannan umarni.

A watan da ya gabata ne hafsan sojojin ya rusa dakarun RSF tare da ayyana mayakan a matsayin ‘yan tawaye bayan da aka gwabza faɗa tsakanin dakarun da ke gaba da juna.

Tuni dai ƙasar ta faɗa cikin tashin hankali da ya janyo mutuwar mutane da dama da kuma raba da yawa da muhallansu.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp