Shugaban kasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya gargadi matukan jiragen yakin Rasha da ke shawagi a cikin kasarsa cewa za su fuskanci shari’a.
Zelensky ya yi wannan kashedin ne a ranar Laraba kamar yadda kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito.
A matsayin misali, ya ambaci wani jirgin yakin Rasha da sojojin Ukraine suka harbo a kan birnin Mariupol da aka yi wa kawanya.
Ya ce, “Kuma wannan zai faru ga duk wanda ya kashe mutanenmu, mutane masu zaman lafiya a cikin kasarmu mai zaman lafiya,” in ji shugaban na Ukraine.
Ya kara da cewa, bisa dukkan alamu matukan jirgin na Rasha ba su da masaniya kan girman umarnin da suke aiwatarwa.
“Kisan fararen hula laifi ne,” in ji shi.
Ukraine ta yi ikirarin kakkabo jiragen yakin Rasha kusan 100 da masu tayar da bama-bamai, tun bayan da Rasha ta mamaye makwabciyarta ta yamma kusan makonni hudu da suka gabata.
Ba za a iya tabbatar da da’awar da kansa ba.