Shugaba Zelensky ya sake yi wa ƴan ƙsar Ukraine jawabi da rana cewa, inda aka nuna shi sanye da kakin soja maimakon baƙar kwat din da ya saba sanyawa.
A jawabinsa na ɗazun nan ya bayyana yaƙin a matsayi “sautin labulen ƙrfe da ya faɗo yake rufe Rasha daga duniyar da ta ci gaba”. ya na mai cewa “aikin mu shi ne mu tabbatar wannan labulen bai faɗo kan iyakar Ukraine ba.”
Ya kuma yi magana a kan dakatar da ayyuka da aka yi tare da ikirarin cewa, dakarun Ukraine suna samun nasarar kare yankin gabashin Donbas, da kuma yi faɗa a kusa da Kharkiv.
Zelensky ya ce, yankin da ya fi bayar da matsala shi ne Kherson a kudancin ƙasar, inda dakarun Rasha suka nausa arewa daga yankin Crimea da suka mamaye.
A cewar sa, maƙiya na ci gaba da kutsawa cikin yankin, ya kuma bayyana tsananin yaƙin da ake yi a Chernobyl.
Sannan ya yi magana a kan dakarun da aka rasa da kuma sojojin Rasha da aka kama.
Zelensky ya kuma ce, an lalata da yawan jirage da motocin yaƙin Rasha, kuma mun lura cewa hakan ya kaɗa ƴan Rasha da dama.