fidelitybank

Shugaban Turkiyya ya nemi ƴan ƙasarsa su fito su marawa Falasɗinawa baya

Date:

Shugaban Turkiyya Recep tayyip Erdogan, ya yi tir da hare-haren da Isra’ila ta kai cikin dare a Gaza waɗanda ya ce sun “ƙara ta’azzara halin da ake ciki”.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalin X, wanda aka sani a baya da Twitter, shugaban ya nemi ‘yan ƙasarsa su fito zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa.

“A yau, ina gayyatar ‘yan uwana zuwa babban maci don Falasɗinawa a Filin Jirgin Sama na Ataturk, Istanbul, inda za mu nuna goyon bayan Falasɗinawa da babbar murya a hare-haren da Isra’ila ke kai musu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa “dole ne Isra’ila ta koma cikin hankalinta kuma ta dakatar da waɗannan hare-hare”.

Da ma tuni dubban ‘yan Tukriyya suka dinga nuna goyon bayansu ga Falasɗinawan duk ranar Juma’a tun daga fara yaƙin a ranar 7 ga watan Oktoba.

Zuwa yanzu, Isra’ila ta kashe mutum fiye da 7,000 a Zirin Gaza da Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da ta mamaye, a cewar ma’aikatar lafiya ta Falasɗinawa.

Isra’ilar na cewa tana kai harin ramuwar gayya ne bayan mayaƙan Hamas sun tsallaka iyaka tare da kashe mutum 1,400 a ƙasar.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp