Shugaban Turkiyya Recep tayyip Erdogan, ya yi tir da hare-haren da Isra’ila ta kai cikin dare a Gaza waɗanda ya ce sun “ƙara ta’azzara halin da ake ciki”.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalin X, wanda aka sani a baya da Twitter, shugaban ya nemi ‘yan ƙasarsa su fito zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa.
“A yau, ina gayyatar ‘yan uwana zuwa babban maci don Falasɗinawa a Filin Jirgin Sama na Ataturk, Istanbul, inda za mu nuna goyon bayan Falasɗinawa da babbar murya a hare-haren da Isra’ila ke kai musu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa “dole ne Isra’ila ta koma cikin hankalinta kuma ta dakatar da waɗannan hare-hare”.
Da ma tuni dubban ‘yan Tukriyya suka dinga nuna goyon bayansu ga Falasɗinawan duk ranar Juma’a tun daga fara yaƙin a ranar 7 ga watan Oktoba.
Zuwa yanzu, Isra’ila ta kashe mutum fiye da 7,000 a Zirin Gaza da Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da ta mamaye, a cewar ma’aikatar lafiya ta Falasɗinawa.
Isra’ilar na cewa tana kai harin ramuwar gayya ne bayan mayaƙan Hamas sun tsallaka iyaka tare da kashe mutum 1,400 a ƙasar.