fidelitybank

Shugaban Turkiyya ya nemi ƴan ƙasarsa su fito su marawa Falasɗinawa baya

Date:

Shugaban Turkiyya Recep tayyip Erdogan, ya yi tir da hare-haren da Isra’ila ta kai cikin dare a Gaza waɗanda ya ce sun “ƙara ta’azzara halin da ake ciki”.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalin X, wanda aka sani a baya da Twitter, shugaban ya nemi ‘yan ƙasarsa su fito zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa.

“A yau, ina gayyatar ‘yan uwana zuwa babban maci don Falasɗinawa a Filin Jirgin Sama na Ataturk, Istanbul, inda za mu nuna goyon bayan Falasɗinawa da babbar murya a hare-haren da Isra’ila ke kai musu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa “dole ne Isra’ila ta koma cikin hankalinta kuma ta dakatar da waɗannan hare-hare”.

Da ma tuni dubban ‘yan Tukriyya suka dinga nuna goyon bayansu ga Falasɗinawan duk ranar Juma’a tun daga fara yaƙin a ranar 7 ga watan Oktoba.

Zuwa yanzu, Isra’ila ta kashe mutum fiye da 7,000 a Zirin Gaza da Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da ta mamaye, a cewar ma’aikatar lafiya ta Falasɗinawa.

Isra’ilar na cewa tana kai harin ramuwar gayya ne bayan mayaƙan Hamas sun tsallaka iyaka tare da kashe mutum 1,400 a ƙasar.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp