Shugaban sojin Isra’ila ya yi murabus daga mukaminsa, saboda abin da ya kira gazawarsa a harin ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta kai cikin kasar, wanda kuma shi ne sanadiyyar yakin Gaza.
Cikin wata wasika da ya aike wa ministan tsaron kasar, Laftnar Janar Herzi Halevi ya amince cewa rundunar sojin Isra’ila, IDF, ta ”Gaza aiwatar da hakkin da ya rataya a kanta na kare ‘yan Isra’ila”
“Gazawata da ta janyo wannan mummunan abu a kullum yana ta bibiyata, kuma zan ci gaba da nadama har karshen rayuwata,” in ji shi.
Jim kadan bayan aika wasikar tasa, sai shugaban rundunar IDF mai kula da yankin kudancin kasar, Manjo Janar Yaron Finkelman, shi ma ya ayyana sauka daga mukaminsa, yana mai cewa shi ma ya gaza a hakkin da ya rataya a kansa na kare yammacin Negev da al’ummar yankin.
Saukar jagororin IDF din na zuwa ne kwana uku bayan fara aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta da fara sakin Isra’ilawan da Hamas ta yi garkuwa da su a lokacin harin ranar 7 ga watan Oktoban 2023.