Shugaban Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Gombe, Abdullahi Maikano Umar, ya yi murabus a matsayin shugaban jam’iyyar inda ya sauya sheƙa zuwa APC.
A wata sanarwa ɗauke da sa hannun tsohon shugaban, ya bayyana cewa rashin manufa ta siyasa ta ɗan takarar jam’iyyar ta NNPP a jihar ne ya sa ya fita daga jam’iyyar domin a cewarsa, bai ga alamun yadda ɗan takarar jam’iyyar Khamisu Mailantaerki zai ciyar da jihar Gombe gaba ba.
Karanta Wannan: Zan ruguza PDP da ‘yan cikinta – Dan PDP a jawabin taron nnpp
“Ba zan zauna wurin da ƙarerayi ne ke zama a kan gaba ba a wurin yaƙin neman zaɓe a maimakon a rinƙa magana a kan hanyoyin ci gaba na gwamnati,” in ji Abdullahi Maikano.
Haka kuma an ga hoton tsohon shugaban na NNPP da Gwamnan Jihar Gombe Inuwa Yahaya.