fidelitybank

Shugaban NLC zai bayyana a gaban ƴansanda yau sakamakon zargin ɗaukar nauyin ta’addanci

Date:

A yau ne Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago, Joe Ajaero, zai amsa gayyatar ƴan sanda domin amsa wasu tambayoyi game da zarginsa da ɗaukar nauyin ta’addanci da laifukan kafofin sadarwa da cin amanar ƙasa da sauransu.

A ranar Talatar ta da gabata ne wato 20 ga watan Agusta ƴan sandan suka gayyaci shi ya bayyana a gabansu bayan wani samame da suka kai a sakatariyar NLC da ke Abuja.

Amma shugaban NLC ɗin ya bayyana cewa zai mutunta gayyatar a ranar Alhamis, 29 ga watan Agustan, maimakon ranar da ƴansandan suka buƙata da farko.

“Ƴan sandan sun ce sun yi samamen ne domin gano wasu muhimman abubuwa da suke da alaƙa da zanga-zangar matsin rayuwa da aka yi a Najeriya,”

Domin nuna goyon baya ga Ajaero, Ƙungiyar Ƙwadago ta umarci mambobinta a faɗin ƙasar da su taru a hedkwatar ƴan sanda na jihohinsu, “har sai shugabansu ya bar hedkwatar ƴan sandan.”

Ƙungiyar Ƙwadagon dai a makon da ya gabata ta yi gargaɗi tare da yin barazanar fara yajin aikin sai baba-ta-gani, idan har aka kama shugabanta, Joe Ajaero.

Idan ba a manta ba, dubban mutane ne suka fito suka yi zanga-zangar matsin rayuwa, ƙarƙashin jagorancin wata ƙungiya mai suna Coalition of Concerned Nigerian Citizens.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp