fidelitybank

Shugaban NLC bai amsa gayyatar ‘yansanda ba

Date:

Shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Joe Ajaero, ya bayyana cewa zai mutunta gayyatar da rundunar ‘yan sanda ta yi masa a ranar Laraba 29 ga watan Agustan 2024, maimakon yau Talata 20 ga watan Agustan 2024 kamar yadda aka buƙata tun farko.

A cikin wata wasiƙa da shugaban ƙwadagon ya aika wa ƴansanda ta hannun lauyoyinsa, Ajaero ya bayyana cewa, wasikar gayyatar ta same shi ne a jiya Litinin, kuma shugaban yana da wasu ayyukan da ya tsara gudanarwa a yau Talata.

Sai dai sanarwar ta ce Ajaero a shirye yake ya amsa gayyatar a ranar Laraba.

Bugu da kari, Ajaero ya buƙaci ƴansanda da su bayar da cikakkun bayanai game da zargin da ake yi masa, waɗanda suka haɗa da samar da kuɗaɗen tallafa wa ayyukan ta’addanci da haɗa baki wajen aikata laifuffuka da cin amanar ƙasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan intanet.

Wasiƙar ta ambato sashe na 36 na kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya bai wa wanda ake tuhuma ƴancin samun cikakken bayani game da yanayi da takamaiman zarge-zargen da ake yi masa.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp