Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a ƙssar nan, ta buƙaci shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas su bayyana ”haƙiƙanin kuɗin gudanarwar” da ake bai wa mambobin majalisun biyu a kowane wata.
Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Lahadi ta buƙaci shugabannin majalisun biyu su bayyana mata cikakkun bayanan kuɗin da majalisun biyu ke kashewa a matsayin kuɗin gudanarwa.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan ƙasar ke ci gaba da tafka muhawara kan yawan kuɗin gudanarwa da ake bai wa ‘yan majalisar dokokin ƙasar a kowane wata.
A makon da ya gabata ne tsohon shugaban ƙasar, Olusegun Obasanjo ya zargi ‘yan majalisar da yanka wa kansu albashi da alawus -alawus a ƙasar.
Lamarin da ya haifar da zazzafar muhawara tsakanin ‘yan ƙasar, inda har wasu ‘yan majalisar dokokin ƙasar suka bayyana abin da ake biyansu.
Ko a makon da ya kamata ma, Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila daga jihar Kano, ya shaida wa BBC cewa ana biyansa naira miliyan 21 a kowane wata a matsayin kuɗin gudanarwar ofishinsa.
Yayin da ya ce yana karɓar albashin da bai kai naira miliyan guda ba a kowane wata.
Ƙungiyar ta Serap ta kuma yi kira ga jagororin majalisar dokokin ƙasar su dakatar da yanka wa kansu albashi da alawu-alawus da sunan kuɗin gudanarwar, kamar yadda aka yi zargi.
Haka kuma ƙungiyar ta kira da a daina sanya wa ‘yan majalisar kuɗin gudanarwar da ake zargi cikin asusun ajiyarsu na banki, kai tsaye, bayan da ta yi zargin cewa suna amfani da kuɗin ta hanyar da ba ta dace ba.
Tana mai cewa rashin sanya kuɗin a asusun ‘yan majalisun zai bai wa hukumomin yaƙi da cin hanci damar gudanar da bincike idan buƙatar hakan ta taso.