fidelitybank

Shugaban majalisu ku bayyana mana kuɗaɗen gudanarwar ku na wata-wata kowa ya sani – SERAP

Date:

Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a ƙssar nan, ta buƙaci shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas su bayyana ”haƙiƙanin kuɗin gudanarwar” da ake bai wa mambobin majalisun biyu a kowane wata.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Lahadi ta buƙaci shugabannin majalisun biyu su bayyana mata cikakkun bayanan kuɗin da majalisun biyu ke kashewa a matsayin kuɗin gudanarwa.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan ƙasar ke ci gaba da tafka muhawara kan yawan kuɗin gudanarwa da ake bai wa ‘yan majalisar dokokin ƙasar a kowane wata.

A makon da ya gabata ne tsohon shugaban ƙasar, Olusegun Obasanjo ya zargi ‘yan majalisar da yanka wa kansu albashi da alawus -alawus a ƙasar.

Lamarin da ya haifar da zazzafar muhawara tsakanin ‘yan ƙasar, inda har wasu ‘yan majalisar dokokin ƙasar suka bayyana abin da ake biyansu.

Ko a makon da ya kamata ma, Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila daga jihar Kano, ya shaida wa BBC cewa ana biyansa naira miliyan 21 a kowane wata a matsayin kuɗin gudanarwar ofishinsa.

Yayin da ya ce yana karɓar albashin da bai kai naira miliyan guda ba a kowane wata.

Ƙungiyar ta Serap ta kuma yi kira ga jagororin majalisar dokokin ƙasar su dakatar da yanka wa kansu albashi da alawu-alawus da sunan kuɗin gudanarwar, kamar yadda aka yi zargi.

Haka kuma ƙungiyar ta kira da a daina sanya wa ‘yan majalisar kuɗin gudanarwar da ake zargi cikin asusun ajiyarsu na banki, kai tsaye, bayan da ta yi zargin cewa suna amfani da kuɗin ta hanyar da ba ta dace ba.

Tana mai cewa rashin sanya kuɗin a asusun ‘yan majalisun zai bai wa hukumomin yaƙi da cin hanci damar gudanar da bincike idan buƙatar hakan ta taso.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp