Gwamnatin Nijar ta saki wasu shugabannin ƴan bindiga ciki har da kwamandojin Boko Haram, ƙarƙashin wani shiri na sulhu a ƙasar.
Shugaba Bazoum ne ya sanar da matakin a ranar Juma’a a wani taron tsaro tare da jami’an soji da na gwamnatinsa da sarakunan gargajiya, kamar yadda kafar talabijin ɗin ƙasar ta ruwaito.
“Akwai shugabannin ƴan ta’adda guda tara, An ba mu shawarar mu sake su, waɗanda kuma na gana da su a fadar shugaban ƙasa saboda ina neman zaman lafiya, kamar yadda aka ambato shugaba Bazoum na cewa.
Wasu mjiyoyin gwamnati sun ce wannan ne karon farko da aka fito aka bayyana sakin waɗanda ake zargi da ta’addanci a Nijar.
Nijar ta daɗe tana fama da hare-hare daga mnayaƙan IS a yammaci da Boko Haram da Iswap da yankin kudu maso gabashi kusa da kan iyaka da Najeriya