Shugaban ƙaramar hukumar Lokoja a jihar Kogi, Muhammed Danasabe ya rasu.
Danasabe ya rasu ne da safiyar ranar Juma’a, a wani asibitin Lokoja bayan wata gajeriyar rashin lafiya.
Mutuwar tasa, na zuwa ne sa’o’i 24 kafin gudanar da zaɓen gwamna a jihar.
Jaridar Vanguard a Najeriya ta ambato wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na jam’iyyar APC a Lokoja, Talba Lakwaja, da ke tabbatar da mutuwar shugaban ƙaramar hukumar.
“Wannan shi ne don sanar wa da jama’a cewa za a binne gawar shugaban ƙaramar hukumar Lokoja, Hon. Mohammed Dasebe Mohammed a maƙabartar Anguwan Kura da karfe 2 na rana bayan sallar Juma’a.
“Za a ɗauki gawar tasa daga gidan danginsa zuwa babban masallacin Lokoja da karfe 1:30 na rana,” in ji sanarwar.