Shugaban ƙasar Jamus, Frank-Walter Steinmeier na ziyarar aiki a Najeriya.
Mista Steinmeier ya isa Najeriya ranar Talata da daddare, nda ya samu tarbar ministan Abuja, Nyesom Wike bayan saukarsa a filin jirgin saman Abuja.
A ziyarar da ake sa ran ta kwana uku ce, Shugaban na Jamus zai gana da Shugaba Bola Tinubu na Najeriya da kuma shugaban hukumar Ecowas, Alieu Omar Touray a Abuja.
Daga nan Mista Steinmeier zai wuce birnin Legas inda zai gana da wakilan kasuwanci da jami’an ƙungiyoyin fararen hula da na al’adu, ciki har da Farfesa Wole Soyinka, kamar yadda gidan Talbijin na Channels ya ruwaito.