fidelitybank

Shugaban Iran ya sallama Mataimakinsa bisa yawon shaƙatawa da ya tafi da Matarsa

Date:

Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya sallami ɗaya daga cikin mataimakansa saboda wata tafiya shaƙatawa zuwa Antarctica da ya yi tare da matarsa Nowruz.

Shugaban ya sallami mataimakin nasa ne saboda abin da ya bayyana da “almubazzaranci” da kuɗi.

Ofishin shugaban ƙasar ya ce tafiya ta mataimakin shugaban ƙasa Shahram Dabiri “ba ta dace ba a daidai lokacin da Iran ke fama da matsain tattalin arziki, kuma ƙasar ba za ta aminta ba.”

An ta yaɗa hotunan Dabiri da matarsa ne suna shaƙatawa a kafofin sadarwa a Iran, inda suka jawo ce-ce-ku-ce da suka a tsakanin al’ummar ƙasar.

Pezeshkian ya ce ya sallami Dabari a matsayin mataimakin shugaban ƙasa mai kula da harkokin majalisa saboda “‘almubazzaranci’ wajen kashe kuɗi, ko da kuwa daga aljihunsa ya ɗauki nauyin zuwa shaƙatawar.

“A gwamnatin da ke bin tafarkin imam na farko na Shia wato Imam Aali, tafiyar da za a kashe maƙudan kuɗi ba ta dace ba ga jami’in gwamnatin ko da kuwa daga aljihunsa ya kashe kuɗin,” in ji Pezeshkian

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp