Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Yakubu Mahmood, ya yi watsi da rahotannin da ke cewa, zai iya tsayawa takarar Shugaban kasa a 2023.
Kungiyar Marubuta Kare Hakkokin Dan Adam ta Najeriya, a ranar Asabar, ta bukaci ‘yan Najeriya da kada su yi mamaki idan shugaban INEC ya sayi fom din fayyace sha’awa da tsayawa takara na Naira miliyan 100, bayan an siyo fom din ga Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele.
Sai dai a wata sanarwar manema labarai da babban sakataren yada labaran sa, Rotimi Yekanmi ya fitar a ranar Lahadi, shugaban na INEC ya bayyana cewa, ba ya sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa, yana mai cewa hakan ba zai faru ba.
Sanarwar mai taken ‘Kira ga shugaban INEC da ya shiga zaben shugaban kasa a 2023’ ya kara da cewa, “Hankalin mu ya karkata ne ga munanan kalamai a wasu wurare cewa kada ‘yan Najeriya su yi mamaki idan shugaban INEC ya shiga takarar shugaban kasa ko kuma ya bukace shi da ya yi hakan. Shawara ce ta rashin gaskiya. Ba zai faru ba.