fidelitybank

Shugaban INEC ka yi murabus kawai – Melaye

Date:

Daya daga cikin masu magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Atiku, Okowa, Sanata Dino Melaye, ya dage cewa dole ne shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, Mahmood Yakubu ya yi murabus.

Tsohon dan majalisar ya bayar da wannan bukata ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Asabar.

Kiran na Melaye na zuwa ne a kan sakamakon barazanar karar da Yakubu ya yi a kan zargin tafka magudi a zaben shugaban kasa da jam’iyyar PDP ta yi.

Karanta Wannan: INEC na amfani da karfin tuwo ga wasu mutane – Dan Takarar Gwamnan NNPP

Idan dai ba a manta ba jam’iyyar ta bukaci ‘yan sanda da hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, da su binciki shugaban hukumar ta INEC kan zargin magudin sakamakon zabe.

PDP ta yi zargin cewa INEC ta yi wa ‘yan Najeriya zagon kasa a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka kammala ranar 25 ga watan Fabrairu.

Sai dai Sakataren Yada Labarai na Yakubu, Rotimi Oyekanmi ya ce kiran bai yi daidai ba kuma ya kalubalanci PDP da ta tabbatar da ikirarin ta a kotun shari’a.

Ya yi mamakin dalilin da ya sa jam’iyyar ta ki bayar da hujjojin da za su tabbatar da zarge-zargen da ake yi, inda ya kara da cewa hukumar zabe ba ta magudin zabe.

Sai dai har yanzu bai gamsu ba, Sanata Melaye ya dage kan cewa dole Yakubu ya tafi, yana mai zargin cewa “ya kula da wata sana’ar aikata laifuka yahoo yahoo INEC.”

“Dole ne Farfesa Mahmud Yakubu yayi murabus. Irin wannan matakin na aikata laifuka & rashin hukunta shi yana zubar da bin doka da kuma rage shi a matsayin alkalin wasa wanda ya ci kwallo a wasa. Mahmood dole gooo,” ya wallafa a shafinsa na twitter.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp