Shugaban hukumar Alhazai ta ƙasa, NAHCON, ya taya Musulman Najeriya murnar zagayowar ranar Eid-el-Fitr na bana.
A sakon taya murna da ya sanya wa hannu, kuma ya aikawa manema labarai, ya godewa Allah Madaukakin Sarki, bisa ganin wannan rana.
“Ina addu’ar cewa, mun fita daga watan Ramadan da daukaka fiye da lokacin da muka fara. Ina kuma rokon Allah Madaukakin Sarki Ya biya mana bukatunmu da muka yi wa kanmu da kasarmu. Allah ya sakawa dukkan ibadun mu da jannatul firdaus,” inji shi