fidelitybank

Shugaban EFCC ya samu sabon muƙami a yankin Afrika

Date:

A wani sabon yunkuri na karfafa tsaro da yaki da cin hanci da rashawa a yankin yammacin Afirka, hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta yi kira da a kara karfi da kuma inganta hanyoyin da za a bi wajen dakile yawaitar safarar kudaden haram da sauran almundahana a yankin.

Shugaban Hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa ne ya yi wannan kiran a ranar Litinin, 21 ga Maris, 2020, yayin da yake jawabi a taron shekara-shekara karo na 5 na cibiyar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa a yammacin Afirka, NACIWA, wanda aka gudanar a Transcorp Hilton Hotel, Abuja, Najeriyaa.

Bawa, wanda shi ne zababben shugaban kungiyar mai wakilai 16, ya yi nuni da cewa, yankin na ECOWAS na da wayo daga matsalolin tsaro da ake fama da shi, ya kuma jaddada cewa, dole ne a yi kokarin dakile zarge-zargen da ke tasowa daga hada-hadar kudade ta haramtacciyar hanya.

“Yankin ECOWAS na fuskantar barazanar kalubalen tsaro wanda ba zai rasa nasaba kai tsaye ko a kaikaice da cin hanci da rashawa ba. Domin haka dole ne mu kara himma wajen dakile tabarbarewar hada-hadar kudi a yankin da suka hada da haramtattun mutane da aka fallasa a siyasance (PEPs),” in ji shi.

Shugaban na EFCC ya kuma jaddada cewa, “Dole ne mu ci gaba da inganta hadin gwiwa da musayar bayanan sirri a kokarinmu na kawar da laifuffukan kudi na yankin tare da magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin”.

NACIWA, wadda ta fito da mambobinta daga kasashe 16 na kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afrika, ECOWAS, na gudanar da wani taron yini biyu da hukumar EFCC da hukumar yaki da cin hanci da rashawa, ICPC, suka shirya a Abuja . A wajen taron, an zabi Bawa gaba daya a matsayin shugaban kungiyar domin ya gaji shugaba mai barin gado, Francis Ben Kaifala, shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Saliyo, wanda wa’adinsa na shekaru uku ya kare a ranar 31 ga Maris, 2022.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp