fidelitybank

Shugaban EFCC ya samu sabon muƙami a yankin Afrika

Date:

A wani sabon yunkuri na karfafa tsaro da yaki da cin hanci da rashawa a yankin yammacin Afirka, hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta yi kira da a kara karfi da kuma inganta hanyoyin da za a bi wajen dakile yawaitar safarar kudaden haram da sauran almundahana a yankin.

Shugaban Hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa ne ya yi wannan kiran a ranar Litinin, 21 ga Maris, 2020, yayin da yake jawabi a taron shekara-shekara karo na 5 na cibiyar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa a yammacin Afirka, NACIWA, wanda aka gudanar a Transcorp Hilton Hotel, Abuja, Najeriyaa.

Bawa, wanda shi ne zababben shugaban kungiyar mai wakilai 16, ya yi nuni da cewa, yankin na ECOWAS na da wayo daga matsalolin tsaro da ake fama da shi, ya kuma jaddada cewa, dole ne a yi kokarin dakile zarge-zargen da ke tasowa daga hada-hadar kudade ta haramtacciyar hanya.

“Yankin ECOWAS na fuskantar barazanar kalubalen tsaro wanda ba zai rasa nasaba kai tsaye ko a kaikaice da cin hanci da rashawa ba. Domin haka dole ne mu kara himma wajen dakile tabarbarewar hada-hadar kudi a yankin da suka hada da haramtattun mutane da aka fallasa a siyasance (PEPs),” in ji shi.

Shugaban na EFCC ya kuma jaddada cewa, “Dole ne mu ci gaba da inganta hadin gwiwa da musayar bayanan sirri a kokarinmu na kawar da laifuffukan kudi na yankin tare da magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin”.

NACIWA, wadda ta fito da mambobinta daga kasashe 16 na kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afrika, ECOWAS, na gudanar da wani taron yini biyu da hukumar EFCC da hukumar yaki da cin hanci da rashawa, ICPC, suka shirya a Abuja . A wajen taron, an zabi Bawa gaba daya a matsayin shugaban kungiyar domin ya gaji shugaba mai barin gado, Francis Ben Kaifala, shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Saliyo, wanda wa’adinsa na shekaru uku ya kare a ranar 31 ga Maris, 2022.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp