fidelitybank

Shugaban ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya rasu

Date:

Shugaban kasar Hadaddiyar Daular Larabawa UAE, Sheikh Khalifa bin Zayed ya rasu a ranar Juma’a, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasar WAM ya ruwaito.

WAM ya ce shugaban ya rasu ne yana da shekara 73 a duniya. In ji BBC.

Tuni kasar ta sanar da makokin kwana 40 inda za a sassauta tutar kasar tun daga ranar Juma’ar 13 ga watan Mayun 2022.

Sannan ta dakatar da aiki a ma’aikatu da hukumomin ƙasar har tsawon kwana uku.

Sheikh Khalifa shi ne sarkin Masarautar Abu Dhabi kuma shugaban ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

A ƙarƙashin kundin tsarin mulkin ƙasar, mataimakin shugaban ƙasa kuma firimiya Sheikh Mohammed bin Rashid al-Maktoum, Sarkin Dubai ne zai zama muƙaddashin shugaban ƙasa.

Amma majalisar tarayya, wadda ta ƙunshi shugabannin masarautun ƙasar bakwai za ta yi wani taro a cikin kwana 30 masu zuwa don zaɓar sabon shugaba.

An haifi Sheikh Khalifa a shekarar 1948, kuma ba a faye ganinsa a bainar jama’a ba tun shekarar 2014 da ya gamu da ciwon zuciya.

Tun a lokacin ƙaninsa da suke uba ɗaya kuma yarima mai jiran gadon masarautar Abu Dhabi Mohammed bin Zayed, da aka fi sani da MbZ, wanda babban abokin Amurka ne, shi ke tafiyar da al’amuran ƙasar.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp