fidelitybank

Shirye-shirye sun yi nisa don shirin gudanar da auren zawarawa — Dr Zahra’u

Date:

 

 

Kwamishiniyar kula da harkokin mata ta Jihar Kano, Dakta Zahra’u Muhammad ta baiyana cewa tuni shirye-shirye sun yi nisa wajen gudanar da shirin nan ba da daɗewa ba.

Ta kuma baiyana cewa Insha Allahu shirin zai gudana ne ta hanyar ma’aikatar kula da mata, inda ta ƙara da cewa kuma za ta zaɓi marayu da marasa galihu a sanya su a cikin shirin.

Dakta Zahra’u ta baiyana hakan ne a wata sanarwar da Jami’ar Yaɗa Labaran Ma’aikatar, Bahijja Malam Kabara ta fitar a yau Lahadi.

Sanarwar ta ce Kwamishiniyar ta bayyana hakan ne a yayin wani taron daurin aure na mutane 31 maza da mata, wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha a yau Lahadi.

A cewar ta, matsalar tattalin arziki, sakamakon annobar korona na ɗaya da ga cikin manyan ƙalubalen da su ka sanya a ka samu tsaiko a shirin auren zawarawa da ƴan mata da Gwamnatin Kano ta saba yi.

Daga nan sai ta yi kira ga ma’aurata da su yi biyayya ga juna, kuma su bi ka’idojin aure kamar yadda ya ke a Musulunci.

Kwamishiniyar ta kuma yaba da ƙoƙarin Gidauniyar FOMWAN da DARUL ARQAM da su ka shirya taron, ta re da yin kira ga sauran kungiyoyi masu zaman kansu da su yi koyi da wannan kyakkyawan misali.

 

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp