fidelitybank

Shirye-shirye sun yi nisa don shirin gudanar da auren zawarawa — Dr Zahra’u

Date:

 

 

Kwamishiniyar kula da harkokin mata ta Jihar Kano, Dakta Zahra’u Muhammad ta baiyana cewa tuni shirye-shirye sun yi nisa wajen gudanar da shirin nan ba da daɗewa ba.

Ta kuma baiyana cewa Insha Allahu shirin zai gudana ne ta hanyar ma’aikatar kula da mata, inda ta ƙara da cewa kuma za ta zaɓi marayu da marasa galihu a sanya su a cikin shirin.

Dakta Zahra’u ta baiyana hakan ne a wata sanarwar da Jami’ar Yaɗa Labaran Ma’aikatar, Bahijja Malam Kabara ta fitar a yau Lahadi.

Sanarwar ta ce Kwamishiniyar ta bayyana hakan ne a yayin wani taron daurin aure na mutane 31 maza da mata, wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha a yau Lahadi.

A cewar ta, matsalar tattalin arziki, sakamakon annobar korona na ɗaya da ga cikin manyan ƙalubalen da su ka sanya a ka samu tsaiko a shirin auren zawarawa da ƴan mata da Gwamnatin Kano ta saba yi.

Daga nan sai ta yi kira ga ma’aurata da su yi biyayya ga juna, kuma su bi ka’idojin aure kamar yadda ya ke a Musulunci.

Kwamishiniyar ta kuma yaba da ƙoƙarin Gidauniyar FOMWAN da DARUL ARQAM da su ka shirya taron, ta re da yin kira ga sauran kungiyoyi masu zaman kansu da su yi koyi da wannan kyakkyawan misali.

 

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp