fidelitybank

Shirin Idon Mikiya: SERAP za ta daukin matakin shari’a a kan Buhari

Date:

Ƙungiyar yaki da rashawa ta SERAPta ce za ta ɗauki matakin shari’a a kan hukumar kula da kafofin yada labarai ta ƙasa (NBC) idan ba ta janye tarar Naira miliyan 5 da ta sanya wa gidan rediyon Vision FM ba da ke Abuja wato cikin awa 24.

A cewar BBC, hukumar ta NBC ta ci tarar gidan rediyon kuma ta dakatar da wani shirinsu mai suna Idon Mikiya na tsawon wata 6, saboda tattaunawar da suka yi kan tsawaita wa’adin Rufai Abubakar, shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta kasa wato National Intelligence Agency (NIA).

NBC ta rubuta wa hukumar Vision FM don sanar da su dokokin yaɗa labarai na Najeriya da suka karya da kuma dakatar da shirin na ‘idon Mikiya’.

Da take mayar da martani ranar Laraba, SERAP ta bayyana matakin na NBC da cewa “ya saba wa kundun tsarin mulki kuma ya saɓa wa doka”, sannan ta yi barazanar kai karar su gaban kotu tare da gwamnatin tarayya idan har ba su ɗage dakatarwar ba da kuma janye kudin tarar nan da awa 24.

“Wannan matakin da gwamnatin Buhari da NBC suka dauka, wani yunƙuri ne na hukumomin ƙasar wajen rufe bakin kafofin yada labarai masu zaman kansu tare da ‘yancin faɗar ra’ayi,” a cewar SERAP cikin wata sanarwa da ta wallafa a Facebook.

“Dole ne gwamnatin ta janye dakatarwar ta kuma bi kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da kuma nauyin da ke kan kasashe don girmamawa da kare hakkin ‘yancin fadin albarkacin baki da samun damar bayanai da kuma yancin yada labarai.

“Wannan wata gazawa ce ga gwamnatin Najeriya wajen kare ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ba wa kafofofin yada labarai masu zaman kansu damar gudanar da ayyokansu a kasar.”

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp