Shugaban hukumar lafiya ta duniya ya ce dakatar da ba da tallafi ga ƙasashen duniya da gwamnatin Trump ta yi na haifar da gagarumar koma-baya.
Yayin da yake jawabi a birnin Geneva, Mista Ghebreyesus ya buƙaci gwamnatin Amurka ta sake duba batun.
Dakta Ghebreyesus ya ce hakan ya shafi yaƙin da ake da cuta mai karya garkuwar jiki da polio da ƙyadar biri da murar tsintsaye.
A farkon makon da ya gabata ne dai gwamnatin Trump ta sanar da dakatar da bayar da tallafi ga ƙasashen waje da wasu ƙungiyoyi, ciki har da hukumar tallafa wa ƙasashe ta Amurka, USAID.
Mista Ghebreyesus ya kuma ce dakatar da tallafin zai shafi ƙoƙarin yaƙi da cuta mai karya garkuwar jiki ta HIV a ƙasashe 50 na duniya.