Gwamna Seyi Makinde ya ce, shirye-shiryen gwamnatinsa na inganta filin tashi da saukar jiragen sama na Ibadan zuwa matsayin kasa da kasa na kan gaba.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Taiwo Adisa ya fitar a Ibadan ranar Lahadi.
Makinde ya bayyana haka ne a yayin bikin yin ritaya da aka gudanar a filin jirgin sama don karrama manajan filin jirgin na Ibadan, Tega Aiyenuro.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan sa, Segun Ogunwuyi, ya ce, gwamnatinsa ta dauki filin jirgin saman a matsayin babban burinta na fadada tattalin arzikin jihar.
Ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da hada kai da masu ruwa da tsaki don ganin an samu nasarar wannan harkar.
Da yake magana a madadin hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa (FAAN), darakta a hukumar, Sunday Ayodele, ya ce, filin jirgin na Ibadan zai inganta habaka tattalin arzikin jihar.