fidelitybank

Shin Tinubu zai amsa kiran majalisa kuwa cikin gaggawa ya mika kasafin 2025?

Date:

Majalisar wakilai ta ja hankalin shugaban kasa Bola Tinubu, kan yiyuwar karya tanadin dokar kashe kuɗin ƙasa idan har ya yi jinkirin gabatar da kasafin kuɗn 2025 ga majalisa.

Wannan na zuwa ne yayin da ya rage watanni biyu wa’adin kasafin 2024 ya ƙare.

Ɗan majalisar da ya gabatar da ƙudirin, Clement Jimbo, ya ja hankali cewa ya kamata a ce kawo yanzu an gabatar da kasafin kuɗin 2025 kasancewar watanni biyu kacal suka rage kafin wa’adin kasafin kuɗin bana ya ƙare.

Majalisar wakilan ta bayyana damuwa a kan ƙurewar lokacin da ya kamata a samu domin nazari kan kasafin na baɗi kafin amincewa da shi a majalisar dokokin tarayya.

Majalisar ta yi nuni da cewa doka ta buƙaci a gabatar wa majalisa ƙiyasin kasafin kuɗi aƙalla watanni huɗu kafin shiga sabuwar shekara domin samun damar tantancewa shi da kuma amincewa.

A yanzu dai majalisar ta miƙa wannan batu ga kwamitinta a kan tsare-tsaren ƙasa.

A ranar biyu ga watan Oktoba shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa Birtaniya domin yin hutun makonni biyu.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp