fidelitybank

Shin Tinubu zai amsa kiran majalisa kuwa cikin gaggawa ya mika kasafin 2025?

Date:

Majalisar wakilai ta ja hankalin shugaban kasa Bola Tinubu, kan yiyuwar karya tanadin dokar kashe kuɗin ƙasa idan har ya yi jinkirin gabatar da kasafin kuɗn 2025 ga majalisa.

Wannan na zuwa ne yayin da ya rage watanni biyu wa’adin kasafin 2024 ya ƙare.

Ɗan majalisar da ya gabatar da ƙudirin, Clement Jimbo, ya ja hankali cewa ya kamata a ce kawo yanzu an gabatar da kasafin kuɗin 2025 kasancewar watanni biyu kacal suka rage kafin wa’adin kasafin kuɗin bana ya ƙare.

Majalisar wakilan ta bayyana damuwa a kan ƙurewar lokacin da ya kamata a samu domin nazari kan kasafin na baɗi kafin amincewa da shi a majalisar dokokin tarayya.

Majalisar ta yi nuni da cewa doka ta buƙaci a gabatar wa majalisa ƙiyasin kasafin kuɗi aƙalla watanni huɗu kafin shiga sabuwar shekara domin samun damar tantancewa shi da kuma amincewa.

A yanzu dai majalisar ta miƙa wannan batu ga kwamitinta a kan tsare-tsaren ƙasa.

A ranar biyu ga watan Oktoba shugaba Tinubu ya bar Najeriya zuwa Birtaniya domin yin hutun makonni biyu.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp