Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban taron jami’ar ne Shugaba Tinubu zai zaɓi wanda zai zama mataimakinsa a zaɓen 2027.
Mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata hira ta musamman da ya yi da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.
A baya-bayan nan, rashin jituwa na neman ɓullowa a APC kan wanda zai yi wa Tinubu mataimaki, bayan da gwamnonin APC suka amince da shugaban ƙasar a matsayin ɗan takarar jam’iyyar a 2027.
A ƙarshen mako ne dai aka kusa bai wa hamata iska a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na shiyyar arewa maso gabas, bayan da wasu ƴan jam’iyyar suka zargi wasu jagorin jam’iyyar da rashin ambatar sunan Kashim Shettima a lokacin da suke jawabin amince wa da Tinubu a matsayin ɗan takarar.
To sai dai tun bayan faruwar lamarin, ba a ji ta bakin fadar shugaban ƙasar ba, lamarin da ya sa wasu ke ganin akwai shirin janye Kashim ɗin daga takarar 2027.
To amma Bayo Onanuga ya musanta wannan zargi yana mai cewa lokaci ne bai yi ba.
“A tsarin takarar shugaban ƙasa, ana fara tsayar da ɗan takara, daga baya sai a zaɓi wanda zai zama mataimakinsa. Haka aka yi lokacin Buhari, an fara tsayar da shi, daga baya ya zaɓi mataimakinsa. Ba a yin su duka lokaci guda,” in ji Onanuga.
A lokacin da yake gwamnan Legas dai, sau kusan uku Tinubu yana sauya mataimaki, abin da ya sa wasu ke ganin zai yi amfani da wancan salo a wannan karon.
To amma Onanuga ya ce, wannan hasashen mutane ne kawai.
“Wannan hasashe ne kawai. Eh, lokacin yana gwamna akwai wasu matsaloli. A wa’adin farko, shi da mataimakiyarsa Kofo ba su jitu ba, hakan ya sa ta bar aiki. Femi Pedro ne ya maye gurbinta. A wa’adinsa na biyu kuma ya ci gaba da aiki da Pedro, sai dai daga baya Pedro ya sauya sheƙa saboda yana so ya tsaya takarar gwamna, wannan ne dalilin barinsa.” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Don haka, ba daidai ba ne a ce Tinubu yana da ɗabi’ar sauya mataimakansa.