fidelitybank

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Date:

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban taron jami’ar ne Shugaba Tinubu zai zaɓi wanda zai zama mataimakinsa a zaɓen 2027.

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata hira ta musamman da ya yi da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.

A baya-bayan nan, rashin jituwa na neman ɓullowa a APC kan wanda zai yi wa Tinubu mataimaki, bayan da gwamnonin APC suka amince da shugaban ƙasar a matsayin ɗan takarar jam’iyyar a 2027.

A ƙarshen mako ne dai aka kusa bai wa hamata iska a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na shiyyar arewa maso gabas, bayan da wasu ƴan jam’iyyar suka zargi wasu jagorin jam’iyyar da rashin ambatar sunan Kashim Shettima a lokacin da suke jawabin amince wa da Tinubu a matsayin ɗan takarar.

To sai dai tun bayan faruwar lamarin, ba a ji ta bakin fadar shugaban ƙasar ba, lamarin da ya sa wasu ke ganin akwai shirin janye Kashim ɗin daga takarar 2027.

To amma Bayo Onanuga ya musanta wannan zargi yana mai cewa lokaci ne bai yi ba.

“A tsarin takarar shugaban ƙasa, ana fara tsayar da ɗan takara, daga baya sai a zaɓi wanda zai zama mataimakinsa. Haka aka yi lokacin Buhari, an fara tsayar da shi, daga baya ya zaɓi mataimakinsa. Ba a yin su duka lokaci guda,” in ji Onanuga.

A lokacin da yake gwamnan Legas dai, sau kusan uku Tinubu yana sauya mataimaki, abin da ya sa wasu ke ganin zai yi amfani da wancan salo a wannan karon.

To amma Onanuga ya ce, wannan hasashen mutane ne kawai.

“Wannan hasashe ne kawai. Eh, lokacin yana gwamna akwai wasu matsaloli. A wa’adin farko, shi da mataimakiyarsa Kofo ba su jitu ba, hakan ya sa ta bar aiki. Femi Pedro ne ya maye gurbinta. A wa’adinsa na biyu kuma ya ci gaba da aiki da Pedro, sai dai daga baya Pedro ya sauya sheƙa saboda yana so ya tsaya takarar gwamna, wannan ne dalilin barinsa.” in ji shi.

Ya ƙara da cewa: “Don haka, ba daidai ba ne a ce Tinubu yana da ɗabi’ar sauya mataimakansa.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp