fidelitybank

Shettima zai jagoranci tawagar gwamnati zuwa wasan ƙarshe na AFCON

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya umarci mataimakinsa Kashim Shettima ya jagoranci tawagar shugaban ƙasa zuwa wasan ƙashen na gasar Kofin ƙasashen Afirka (Afcon) da ke gudana a ƙasar Ivory Coast.

Cikin wata sanarwar da mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar kan sadarwa, Stanley Nkwocha ya fitar, shugaba Tinubu ya buƙaci tawagar Super Eagles ta Najeriya, ta yi duk mai yiwuwa don sanya ‘yan ƙasar alfahari da tawagar a nahiyar Afirka.

Mataimakin shugaban ƙasar ya wakilci shugaba Tinubu a wasan kusa da na ƙarshe da ƙungiyar ta doke Afirka ta Kudu a tsakiyar mako.

Tawagar ta Najeriya dai za ta yi gumurzu da mai masaukin baƙi, Ivory Coast a wasan ƙarshe ranar Lahadi 11 ga watan Fabrairu.

Ƙasashen biyu dai sun fafata a wasan cikin rukuni a wannan gasar, inda Najeriya ta yi nasara da ci 1-0.

”Ƙwallon ƙafa ke taka rawa wajen haɗa kan ‘yan ƙasa, kuma rawar da tawagar super Eagles ta taka wajen ƙarfafa haɗin kai tsakanin ‘yan Najeriya ya tabbatar da haka”, in Tinubu.

Shugaban na Najeriya ya ce ya yi imanin zuwa wasan ƙarshen da mataimakinsa da sauran ‘yan tawagarsa za su yi, alama ce da ke tabbatar da goyon bayan gwamnatin ƙasar ga tawagar Super Eagles kan sadaukarwa da nasarorin da take yi.

Haka kuma gwamnatin ƙasar ta yi kira ga ‘yan Najeriya da ke ciki da wajen ƙasar da su haɗa kansu wajen nuna goyon baya ga tawagar ƙasar, ta hanyar furta kalaman ƙarfafa wa ‘yan wasan gwiwa, domin samun nasara a wasan.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp