Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya soki sabuwar zaɓabɓiyar ƴar shugabar jam’iyyar Conservative a Birtaniya, Kemi Badenoch saboda kaskantar da Najeriya.
Shettima ya bayyana haka ne ranar Litinin a taron tattaunawa kan hijira karo na 10 da aka yi a Abuja.
Mataimakin shugaban Najeriyar ya ce “Muna alfahari da kasancewar Kemi Badenoch a matsayin shugabar jam’iyyar Conservative a Birtaniya, duk da kaskantar da ƙasarta ta asali da ta ke yi.”
“Tana da damar bayyana ra’ayinta a kan koma mene ne, kai har ma idan tana son cire Kemi a cikin sunanta ma za ta iya, to amma ba wai hakan ba zai rage wa Najeriya matsayinta na kasancewa ƙasar baƙar fata mafi shahara ba.”
Ya ce, “Idan ka lura duk inda ka samu baƙar fata uku to ko shakka babu za ka ga ɗaya daga cikinsu ɗan Najeriya ne.”
Daga nan ya jaddada ƙoƙarin gwamnati na kare hakkin ƴan ci-rani da kuma taya su murna a kodayaushe saboda irin ci gaba da ma gudunmawar da suke bayar wa wajen ciyar da ƙasa gaba.
A 2022, Badenoch, wato a lokacin da ta ke a matsayin ƴar majalisar dokokin Birtaniya daga Najeriya wadda kuma ake ganin za ta iya zama Firaiministar Birtaniya wata rana, ta zargi ƴan siyasar Najeriya da amfani da kuɗin al’umma don biyan buƙatun kansu.
Bayan zaɓarta a masatyin shugabar jam’iyyar Conservative a watan Nuwambar 2024, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje NIDCOM, Abike Dabiri-Erewa, ta ce hukumarta ta yi ta tuntuɓar Badenoch, to amma babu wata alama ta nuna cewa ta samu sakon hukumar.