fidelitybank

Shettima ya yi fatali da shugabar jam’iyyar Birtaniya

Date:

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya soki sabuwar zaɓabɓiyar ƴar shugabar jam’iyyar Conservative a Birtaniya, Kemi Badenoch saboda kaskantar da Najeriya.

Shettima ya bayyana haka ne ranar Litinin a taron tattaunawa kan hijira karo na 10 da aka yi a Abuja.

Mataimakin shugaban Najeriyar ya ce “Muna alfahari da kasancewar Kemi Badenoch a matsayin shugabar jam’iyyar Conservative a Birtaniya, duk da kaskantar da ƙasarta ta asali da ta ke yi.”

“Tana da damar bayyana ra’ayinta a kan koma mene ne, kai har ma idan tana son cire Kemi a cikin sunanta ma za ta iya, to amma ba wai hakan ba zai rage wa Najeriya matsayinta na kasancewa ƙasar baƙar fata mafi shahara ba.”

Ya ce, “Idan ka lura duk inda ka samu baƙar fata uku to ko shakka babu za ka ga ɗaya daga cikinsu ɗan Najeriya ne.”

Daga nan ya jaddada ƙoƙarin gwamnati na kare hakkin ƴan ci-rani da kuma taya su murna a kodayaushe saboda irin ci gaba da ma gudunmawar da suke bayar wa wajen ciyar da ƙasa gaba.

A 2022, Badenoch, wato a lokacin da ta ke a matsayin ƴar majalisar dokokin Birtaniya daga Najeriya wadda kuma ake ganin za ta iya zama Firaiministar Birtaniya wata rana, ta zargi ƴan siyasar Najeriya da amfani da kuɗin al’umma don biyan buƙatun kansu.

Bayan zaɓarta a masatyin shugabar jam’iyyar Conservative a watan Nuwambar 2024, shugabar hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje NIDCOM, Abike Dabiri-Erewa, ta ce hukumarta ta yi ta tuntuɓar Badenoch, to amma babu wata alama ta nuna cewa ta samu sakon hukumar.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp