Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bar Abuja zuwa kasar Amurka domin halartar taro na 79 na Majalisar Dinkin Duniya, UNGA, bisa umarnin shugaba Bola Tinubu.
Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa (Ofishin mataimakin shugaban kasa), Mista Stanley Nkwocha, ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Lahadi.
Tun da arko Tinubu ya umurci mataimakin shugaban kasar da ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa babban taron duniya.
A cewar sanarwar, hakan zai baiwa shugaban kasar damar mayar da hankali wajen magance matsalolin cikin gida da suka hada da bala’in ambaliyar ruwa da aka yi a wasu sassan kasar.
Nkwocha ya ce yayin zaman, Shettima zai gabatar da bayanin kasa Najeriya, da halartar muhimman tarukan da ke gefen taron, da kuma yin tarukan kasashen biyu.
Ya ce babban taron wanda ke dauke da taken, ‘Kada a bar kowa a baya: Yin aiki tare don ci gaban zaman lafiya, ci gaba mai dorewa da mutuncin dan’adam na zamani da na gaba’, zai gudana ne daga ranar 24 ga Satumba zuwa 28 ga Satumba.