fidelitybank

Shettima ya tafi Amurka taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bar Abuja zuwa kasar Amurka domin halartar taro na 79 na Majalisar Dinkin Duniya, UNGA, bisa umarnin shugaba Bola Tinubu.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa (Ofishin mataimakin shugaban kasa), Mista Stanley Nkwocha, ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Lahadi.

Tun da arko Tinubu ya umurci mataimakin shugaban kasar da ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa babban taron duniya.

A cewar sanarwar, hakan zai baiwa shugaban kasar damar mayar da hankali wajen magance matsalolin cikin gida da suka hada da bala’in ambaliyar ruwa da aka yi a wasu sassan kasar.

Nkwocha ya ce yayin zaman, Shettima zai gabatar da bayanin kasa Najeriya, da halartar muhimman tarukan da ke gefen taron, da kuma yin tarukan kasashen biyu.

Ya ce babban taron wanda ke dauke da taken, ‘Kada a bar kowa a baya: Yin aiki tare don ci gaban zaman lafiya, ci gaba mai dorewa da mutuncin dan’adam na zamani da na gaba’, zai gudana ne daga ranar 24 ga Satumba zuwa 28 ga Satumba.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maÆ™iya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...
X whatsapp