Majalisar Tattalin arzikin Najeriya na gudanar da wani taro a fadar gwamnati.
Taron na samun halartar shugaban majalisar tattalin arzikin, kuma mataimakin shagaban ƙasar Kashim Shettima, da gwamnonin jihohi 36 waɗanda ke zama mambobin kwamitin.
Rahotonni na cewa taron na samun halartar masu ruwa da tsaki daga bankin Duniya, da sauran hukumomin gwamnatin ƙasar.
Ana sa ran taron zai tattauna batun yadda za a raba tallafin da za a bai wa ‘yan ƙasar, don rage raɗaɗin da cire tallafin man fetur ya haddasa.
An dai samu tashin farashin man fetur a ƙasar bayan cire tallafin, lamarin da ya ƙara ta’azzara tashin farashin kayayyaki a ƙasar.
Shugaban ƙasar Bola Tinubu ne ya sanar da bayar da tallafin domin taimaka wa talakawan ƙasar wajen rage musu raɗaɗin da suke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur ɗin.