Kungiyar Gwamnonin (PGF) ta bayyana Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano a matsayin hasken da ke wakiltar siyasar Najeriya yayin da ya ke murnar cika shekaru 72 da haihuwa.
Gwamna Abubakar Bagudu na jihar Kebbi kuma shugaban kungiyar ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa takwarorinsu na jihar Kano.
PGF wata kungiya ce ta gwamnonin da a ka zaba a karkashin jam’iyyar APC.
Bagudu ya yi murna da Ganduje, inda ya ce shi shugaba ne mai hangen nesa da jajircewa wajen ganin an samu dunkulewar kasa da kasa baki daya.
Ya jaddada kudirin dandalin na aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa karfin jihohi masu ci gaba, domin samar da ayyukan yi da karfafa ayyukan tattalin arziki da rage rashin daidaito da kuma rage talauci.
“Tare da jama’ar jihar Kano, da sauran ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, muna murnar wannan gagarumin biki tare da ku da iyalanku.
“Musamman muna so mu yaba tare da yaba wa jagoranci, hangen nesa da kuma jajircewar ku wajen ganin an samu dunkulewar Nijeriya, a karkashin jagorancin jam’iyyarmu ta APC.
“Muna godiya da irin gudunmawar da ku ka bayar ga tawagarmu ta Gwamnonin ci gaba ta hanyar ba da haske da jajircewa da ku ka bayar wajen tafiyar da harkokin mulki a Jihar Kano da ma a matakin kasa baki daya,” inji Bagudu.
Shugaban PGF ya bayyana cewa a matsayinsa na gwamnan jihar Kano, a duk wasu tsare-tsaren ci gaban da gwamnatin APC ke aiwatarwa, Ganduje ya ci gaba da kasancewa jagora na gaskiya.