Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya taya gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, murnar cika shekaru 62 a duniya.
A wani sakon da ya aike wa Gwamnan, wanda mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu, ya fitar a ranar Asabar a Abuja, shugaba Buhari ya yaba wa Sule bisa mai kishin kasa da kwazon da dogaro da kai wajen mayar da jihar Nasarawa zuwa kasa mai zaman lafiya da ci gaba samar da wadata.
Shugaban ya yabawa gwamnan bisa yadda ya ke gudanar da mulki na gari zuwa yanzu, ya kuma yi fatan ya cika burinsa na ganin jihar Nasarawa ta zamanto mai zaman lafiya da ci gaba, ya kuma zama abin koyi ga sauran mutane.
“Ina fatan ka kasance cikin koshin lafiya kuma ka rayu tsawon lokaci, tare da gama aikin ka na siyasa cikin albarka,” inji Buhari.