Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da sauran manyan baki sun yi kira ga ’ya’yan kungiyar tsofaffin daliban jami’ar Bayero na ɓangaren koyon aikin jarida Mass Communication Association (BUMCAA), da su ci gaba da bayar da goyon baya ga ci gaban sashen da na cibiyar.
Mai martaba Aminu Ado Bayero, wanda kuma ya kammala karatunsa na digiri na biyu a fannin sadarwa na Mass Communication, ajin 1984, ya yi wannan kiran ne a ranar Asabar a Kano, a wata lacca da kungiyar BUMCAA ta shirya, domin bikin cika shekaru 40 da kafuwar zangon farko.
Ya ce, “Ya na da kyau mu ga yadda za mu ci gaba da taimaka wa ɗaliban mu, bisa iyawarmu. Ya kamata mu kuma taimaka wa masu karamin karfi a cikin al’umma,” inji shi.
Sarkin ya bukaci dalibai da tsofaffin daliban da su ci gaba da zama jakadu nagari a duk inda suka samu kansu.
A nasa jawabin, mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya taya sashen murnar nasarar da aka samu.