Shekaru uku cif da mataimakin shugaban kasa, Farfaesa Yemi Osibanjo, ya tsallake rijiya da baya, bayan da wani jirgi mai saukar Ungulu ya yi hatsari a garin Kabba na jihar Kogi.
Hadarin, wanda da ya faru ne a ranar 2 ga watan Fabrairu a lokacin da Farfesa Yemi Osibanjo, ke tafiya yakin neman zaben 2019.
Osinbajo, yayin da ya ke mayar da martani kan lamarin, a shekarar 2019, ya ce, za a iya sanyawa ranar a matsayin ‘ranar bakin ciki’ idan lamarin ya lankwame rayukan su.
“Da an tuna da ni a matsayin ranar bakin ciki, saboda hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu a ranar 2 ga Fabrairu, 2019, wanda ya hada ni da wasu goma sha daya a ciki.
“Amma ina farin ciki kuma mun gode wa Allah da ya zama ranar nasara da godiya,” in ji Osibanjo.
Kasancewar lokacin yakin neman zabe, wasu ‘yan siyasa, musamman ‘yan jam’iyyun adawa sun yi murna da wannan lamari, inda suka yi zargin cewa hukunci ne na gazawar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.