fidelitybank

Shekaru 10 da sace Daliban Chibok: Dalilin da ya sa na auri Dan Boko Haram – Nkeki

Date:

Bayan shekaru 10, Amina Nkeki, daya daga cikin ‘yan mata 276 da aka sace na makarantar sakandaren ‘yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a jihar Borno, ta ce ta auri mayakan Boko Haram ne domin ta samu ‘yanci.

Nkeki, wacce ta samu ‘yanci a shekarar 2016 tare da jariri da kuma mayakan Boko Haram a matsayin mijinta, ta bayyana hakan ne a gidan Talabijin na Channels.

Ta ce wasu abokan aikinta sun haifi ‘ya’ya hudu ga maharan da suka yi garkuwa da su.

Nkeki ta ce ta amince ta auri mayakan Boko Haram ne a lokacin da take garkuwa da su, saboda tana kallon hanyar a matsayin hanyar kubuta daga hannun wadanda suka sace ta.

“A gare ni, na yi aure ne domin in sami ‘yancin zuwa inda nake so kuma daga can zan tsere.”

Ta ce maharan na yi wa ‘yan matan barazanar auren su, ko kuma su zama bayin su har abada.

“Sun gaya mana cewa idan ba mu yarda mu aure su ba, za mu zama bayinsu. Don haka, saboda wannan tsoro, wasunmu suna tunanin maimakon zama bayi, mu yi aure.

“Haka wasu suka yanke shawarar yin aure. Kuma wasu mutane sun dauki duk kasadar. Wasu daga cikinmu sun yi aure wanda zai iya zama hanyar tsira, musamman ma mutum kamar ni,” inji ta.

Dalibai 276 amma ‘yan mata 57 sun tsere jim kadan a shekarar 2014.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp