fidelitybank

Shekarau ya nemi Sanata Hanga ya dakata da neman takarsa

Date:

Ga alama an shiga ruɗani game da takarar sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar NNPP kasancewar bayanai na nuna cewar har yanzu sunan Sanata Malam Ibrahim Shekarau ne a hukumar zaɓe ta INEC.

Wannan na zuwa ne duk da irin ƙokarin da bangaren NNPP din suka yi na ankarar da INEC ɗin tare da rubuta musu takardar cewa sun sauya sunan Malam Shekarau da na Sanata Rufa’i Sani Hanga.

A tattaunawarsa da BBC, Malam Ibrahim Shekarau ya ce shi da kansa ya rubuta wa INEC cewa a sauya sunansa saboda ya bar jam’iyyar, amma sai ta ce masa lokacin canza sunan ɗan takara ya wuce, sai dai, idan ɗan takara ne ya rasu.

Ya ce tuni ya bar jam’iyyar NNPP kuma ba ita yake wakilta ba, inda ya ce ko da ya ci zaɓe ba a cikinta yake ba.

Sanata Shekarau ya kuma ce, ya kira wanda yake takarar kujerar ta sanata a jam’iyyar NNPP, inda ya ce masa ya dakatar da yakin neman zaɓe saboda ba sunan shi ne a jerin sunayen da hukumar zaɓe ta san da su ba.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp