fidelitybank

Shekarau ba ya yi wa Gawuna aiki – Ɗan Takarar Gwamnan PDP

Date:

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano, Sadiq Wali, ya yi zargin cewa yakin neman zabe da ake yi wa Mallam Ibrahim Shekarau wani shiri ne na haifar da rikici a cikin jam’iyyar da kuma raunana ta gabanin zaben gwamna da za a yi a karshen mako mai zuwa.

Shekarau ya sauya sheka daga jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP zuwa PDP a daidai lokacin da ake tunkarar zaben 2023 a karshen shekarar da ta gabata.

Da yake magana a yayin wani taron manema labarai a Kano a daren ranar Alhamis, Wali ya ce babu gaskiya cikin jita-jitar da ake yadawa na cewa Shekarau yana aiki da dan takarar APC a zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 11 ga Maris.

Dan takarar gwamnan na PDP ya jaddada cewa babu shakka zai iya cewa Shekarau yana yi masa aiki domin samun nasarar PDP a jihar.

A cewar Wali, wannan jita-jita ta samo asali ne daga shirun da Shekarau ya yi a rikicin PDP a Kano, domin an yi shari’ar a kotu.

Ya ce: “Ba gaskiya ba ne. Me Shekarau zai amfana da shi idan ya yi wa Gawuna aiki a yanzu? Zan iya fada muku babu shakka Mallam Ibrahim Shekarau ba shi da wata matsala da takara ta. Wai a ce Shekarau yana aiki a karkashin kasa don yakar takarata.

“Kawai dai Shekarau ya yanke shawarar yin shiru a rikicin PDP a matakin jiha, saboda ana shari’ar a kotu. A matsayinsa na mutum mai mutunta doka da dimokuradiyya, bai kamata ya yi magana a kan karar da ke gaban kotu ba. Amma ni a ra’ayina, ba gaskiya ba ne cewa Shekarau yana yi wa APC aiki.”

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp