fidelitybank

shekarar 2023 ce mafi tashin hankali a wajen ‘yan Jarida – MDD

Date:

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan’adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana shekara ta 2023, a matsayin mafi tashin hankali ga aikin jarida, saboda shekara ce da aka kashe ‘yan jarida da ma’aikatan yaɗa labarai har 71 a faɗin duniya.

Babban Kwamishinan Kare Haƙƙin Ɗan’adam na Majalisar Ɗinkin Duniya, Volker Turk ya ce a shekarar an kuma ɗaure ‘yan jarida har 320, adadi mafi yawa da aka taɓa samu.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wani jawabin da ya gabatar, albarkacin Ranar Tunawa da ‘Yancin ‘Yan Jarida ta 2024, wadda ake gudanarwa a yau Juma’a.

Ya ce idan yana tunawa da aƙidojin aikin jarida, yana tunawa ne da amana da gaskiya da tsare ƙima. Yana tuna ɗumbin ɗaiɗaikun mutanen da ba su da tsoro, kuma suna da ƙundumbalar yin tambaya.

Mutane ne masu yin ƙuru wajen ƙalubalantar gwamnati da sanya rayuwarsu cikin kasada wajen tattaro bayanan aika-aikar da aka tafka da cin hanci da wani laifi, da kuma tsayawa haiƙan wajen yaƙi da zalunci.

A cewarsa, idan muka rasa ɗan jarida, mun yi asarar idanuwanmu da kunnuwanmu. Mun rasa murya ga mutanen da ba a jin amonsu.

Haƙiƙanin gaskiya ma dai, mun rasa mai kare haƙƙin ɗan’adam.

Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, an ɓullo da ita ne don tunawa da aƙidar gaskiya da kuma kare mutanen da ke aiki da ƙwarin gwiwa don bankaɗo gaskiya.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp