Kamfanin ƙera mota na Kia ya nada, Shatu Gorko, Sarauniyar Kyau ta Najeriya a matsayin jakadar kamfanin a Najeriya.
Wannan nadin ya biyo bayan kyautar mota samfurin Kia Rio ga sarauniyar wadda matashiya mai shekaru 18, bayan da ta lashe gasar kyau ta Miss Nigeria ta 44 da aka yi a watan Disamba.
Manajan kamfanin Kia a Najeriya ya ce, kamfanin na da zummar ganin mata sun sami daukaka da ci gaba ta hanyar tallafa musu.
Sabuwar jakadiyar kamfanin na Kia, Shatu Garko ta ce “Abin alfahari ne da na zama cikin iyalan kamfanin Kia.”